Rundunar yansandan jihar Jigawa ta kame mutane 20 da take zargi da aikata laifuka daban-daban da suka hada da fashi da makami, garkuwa da mutane da kisan kai, inda ta kwato kayan sata daga hannunsu da kuma makamai.
Kwamishinan yansanda na jiha, Usman Sule Gomna, ya sanar da haka a taron manema labarai a Dutse.
Kwamishinan ya bayyana cewa tawagar yansanda ta musamman masu yaki da fashi da makami sun kai farmaki kan wasu maboyar ‘yan fashi a yankin karamar hukumar Ringim inda suka damke wasu daga cikin ‘yan fashin.
- Akalla mutane 28 ne suka rasa rayukansu sanadiyyar hare-haren ‘yan bindiga a jihar Zamfara
- ‘Yan Kasuwa na nuna damuwar su kan faduwar farashin kayan Abinci
- Gwamnatin Jigawa ta bukaci jama’a da su kai rahoto kan duk dillalin da ke kokarin bata shirin Noma
- Hukumar JAMB ta cire wasu cibiyoyi guda 5 daga jerin wuraren gudanar da jarabawar UTME ta 2025
- Hukumar EFCC na neman jami’an CBEX ruwa a-jallo
Ya kara da cewa jami’an yansanda a karamar hukumar Babura sunyi arangama da wasu yan bindiga 9 a kauyen Andau dake yankin karamar hukumar.
Sule Gomna ya kuma ce tawagar yansanda ta musamman masu yaki da fashi da makami sun kama mutane 10 da ake zargin barayine yan bindiga a kwaryar birnin Dutse.