Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nemi a yi ƙari a kasafin kuɗin da ya gabatar na shekarar 2025 daga naira triliyan 49.7 zuwa naira triliyan 54.2.
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata wasiƙa da shugaban ya aika wa shugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio, wanda ya karanta a zaman majalisar a yau Laraba.
A cikin wasiƙar, shugaban ya ce buƙatar ƙarin ta taso ne sakamakon samun ƙarin kuɗaɗen shiga na naira triliyan 1.4 daga hukumar tattara haraji ta ƙasar FIRS, da naira triliyan 1.2 daga hukumar hana-fasa-ƙwauri ta kwastam, sai kuma naira triliyan 1.8 daga wasu hukumomin gwamnati.
Bayan karanto wasiƙar shugaban ƙasar, shugaban majalisar dattawan ya buƙaci kwamitin da ke kula da kasafin kuɗin kan su gaggauta duba batun.
Ya kuma tabbatar cewa za a kammala dubawa da amincewa da kasafin kudin kafin ƙarshen Fabrairu.