A nan jihar Jigawa, yayinda al’umma ke cikin halin damuwa sakamakon ifti’la’in ambaliyar ruwa da tayi sanadin muhallai da gonakinsu, a kokarin saukaka radadin zukata, sanatan jihar mai wakiltar santoriyar gabas Barrister Ibrahim Hassan, ya bayar da gudun mawar kayayyakin tallafi ga wadanda abin ya shafa a karamar hukumar Kriskasamma.
Da yake mika kayayyakin a madadin Sanatan, shugaban kungiyar yan kasuwar masarautar Hadejia Alhaji Idris Maji Dadin Jabo, yace kayayyakin sun kunshi fatun buhu 100, buhunan gari 5, buhun sukari 2 da kuma tabarmi 120.
- Kungiyar Afenifere ta soki matakin da gwamnatin Tinubu ta dauka kan wakar “Tell Your Papa”
- An bukaci Majalisa ta ware Naira biliyan 2 domin bunkasa magungunan gargajiya a Najeriya
- Rundunar ƴansanda Najeriya za ta hukuta ƴansandan da aka rabawa kuɗi a bidiyo
- Akwai yiwuwar jefa ƴan Najeriya cikin duhu matuƙar gwamnati bata biya bashin Naira Triliyan huɗu ba
- An raba Naira Triliyan 1.57 a tsakanin gwamnatocin tarayya, jihohi da kananan hakumomi a Najeriya – FAAC
Da yake karbar kayayyakin, shugaban karamar hukumar Alhaji Salisu Garba Kubayo, ya yaba da kokarin sanatan, tare da alkauranta rabon kayan a fadin mazabun karamar hukumar 5.
Saurari hirar da wakilinmu yayi da Sanatan da kuma bubuwa da ya fada