Sanata mai wakiltar Jigawa ta Arewa maso Gabas,Brr. Ibrahim Hassan Hadejia ya bada gudunmawar takunkumin rufe hanci da baki guda dubu goma da dari shida da talatin ga makarantu domin rabawa daliban mazabarsa.
Wakilin Sanatan, Muhammad Lawan wanda ya mika gudunmawar kayayyakin yace hakan zai taimaka wajen marawa kudirin gwamnati baya na yaki da yaduwar cutar corona.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Ya kuma bukaci malamai da dalibai dasu yi cikakken amfani da shi wajen kare kai daga kamuwa daga cutar inda kuma ya yabawa ma’aikatar ilmi bisa tsare-tsaren da tayi na samun nasarar rubuta jarabawar karshen ga dalibai.
Kazalika, Sanata Ibrahim Hassan Hadejia ya bada gudunmawar kayayyakin bada horo ga cibiyar rubuta jarabawar kammala sakandare ta NECO dake makarantar sakandaren Famfo Goma.