Ruwan sama kamar da bakin kwarya ya lalata wani bangare na cibiyar lafiya ta garin Saleri dake yankin karamar Hukumar Kirikasamma anan jihar Jigawa.
Manajan Hukumar lafiya matakin farko na yankin Usman Abdullahi Birniwa ya sanar da hakan ga manema labarai a Birniwa.
Yace ruwan saman hade da iska ya lalata sashen kula da mata masu juna biyu da kuma wasu kayayyakin aiki.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Usman Abdullahi yace a yanzu haka ambaliyar ruwa na neman mamaye cibiyar lafiyar inda ya roki gwamnati data kai musu daukin gaggawa.
Tunda farko kamsilan sashen tsare tsare Abdullahi Gada yace karamar hukumar ta bada gudunmawar fatun bahuna 200 domin yin jinga a cibiyar.
Ambaliyar ruwa ta lalata gidaje 46 yayin da kayayyakin amfanin gona na miliyoyin naira suka salwanta a garin na Saleri.