Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a 12 ga watan Yuni a matsayin ranar hutun ranar demokradiyya ta bana.
Ministan cikin gida, Rauf Aregbesola, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa a madadin gwamnatin tarayya.

Sanarwar wacce ke dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Georgina Ehuriah, ta jiyo Aregbesola na taya ‘yan Najeriya murnar dorewar mulkin demokradiyya a kasarnan.
- Akalla mutane 28 ne suka rasa rayukansu sanadiyyar hare-haren ‘yan bindiga a jihar Zamfara
- ‘Yan Kasuwa na nuna damuwar su kan faduwar farashin kayan Abinci
- Gwamnatin Jigawa ta bukaci jama’a da su kai rahoto kan duk dillalin da ke kokarin bata shirin Noma
- Hukumar JAMB ta cire wasu cibiyoyi guda 5 daga jerin wuraren gudanar da jarabawar UTME ta 2025
- Hukumar EFCC na neman jami’an CBEX ruwa a-jallo
Ministan ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su cigaba da godewa kokarin da aka yi wajen dawo da mulkin demokradiyya.
Ya tabbatarwa da ‘yan Najeriya jajircewar gwamnatin tarayya wajen yaki da annobar corona tare da hadin kan dukkan ‘yan Najeriya.