Najeriya ta tsananta tsaro kan iyakokinta saboda cutar Ebola

0 81

Hukumar daƙile yaɗuwar cututtuka a Najeriya NCDC ta tsananta tsaro da sanya ido kan iyakokin shiga ƙasar kamar filayen jiragen sama, domin guje wa shigar cutar Ebola cikin ƙasar.

A cikin wani bayani da shugaban hukumar Dakta Jide idris ya fitar, ya tabbatar da cewa ba a samu wani ɗauke da cutar ba zuwa yanzu.

Hukumar ta kuma gargaɗi ƴan ƙasar su guje wa yin tafiyar da ba ta zame wajibi ba zuwa ƙasashen da aka samu ɓullar cutar.

A ranar 30 ga watan Janairun 2025 ne Uganda ta tabbatar da ɓullar cutar Ebola a biranen Wakiso da Mukono da Mbale da ke yankin Mbale.

Zuwa yanzu dai an tabbatar da mutuwar mutum ɗaya, yayin da hukumomi ke cigaba da sanya ido kan mutane 44 da ake tunanin sun haɗu da wanda ya mutu sanadiyyar cutar.

– BBC Hausa

Leave a Reply