Gwamantin jihar Jigawa ta amince a bude makaratun fririmare da na sakandire a ranar litinin 26 ga watan nan a fadin jiha.
Kwamishinan yada labarai na jihar nan Malam Ibrahim Mamser ne ya bayyana hakan bayan zaman majalissar zartarwa ta jihar da aka gudanar karkasahin gwamna Muhammadu Badaru Abubakar a gidan gwamanti dake dutse.

A tsarin jadawalin komawar, Yan makarantun kwana zasu koma a ranar lahadi 25 ga watan oktoba, sannna bayan kwana daya sauran yan makarantun jeka ka dawo su koma a ranar litinin 26 ga watan nan da muke ciki.
- Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kara filayen noman shinkafa zuwa hekta 500,000 nan da shekarar 2030
- Gwamnomin Jam’iyyar PDP sunyi watsi da shirin yin kawance domin kawar jam’iyyar APC
- Ƴan Nijar mazauna Libya sun buƙaci gwamnatin Nijar ta kai musu ɗauki
- Za a kammala sabunta titin Abuja-Kaduna-Kano cikin wata 14 – Ministan ayyuka
- Gwamnatin Najeriya ta kafa kwamiti don nazarin tasirin sabon harajin Amurka
Sannan ya kara da cewa yaran firimare yan aji 1 zuwa 3 za suna zuwa da safe sannan yan aji 4 zuwa aji 6 zasu na zuwa da yamma.
Kazalika ya kara da cewa yan karamar sakandire zasu na zuwa makarantun su da safe, kana daga bisani yan yan babbar sakandire zasu na zuwa da yamma.