Hukumar samarda aiyukan yi ta kasa NDE ta kaddamar da bada horan watanni uku ga matasa maza da maza guda dari a jihar Jigawa.
Shugaban hukumar a jihar nan Malam Abubakar Jamo ya sanar da hakan a lokacin ganawa da manema labarai a garin Dutse.
Yace wasu daga cikin matasan zasu sami horo akan bangarori daban daban na aikin gona.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Mallam Jamo ya kara da cewar ana gudanar da bada horan ne karkashin shirin bada horo a yankunan karkara.
Inda yace matasan za a tura su wuraren koyan sanin makamar aiki na makonni biyu a gonaki.
Mallam Abubakar Jamo ya shawarci matasa dasu shiga cikin shirin domin samun hanyoyin dogaro da kai.