Shugaba muhammadu Buhari ya taya yan najeriya murna biyo bayan bankwana da kasar tayi daga cutar shan inna, yayin nuna godiyarsa ga wanda suka taimaka na gida dana waje, bisa jajircewarsu na ganin sun raba kasar da cutar yaran.
A jawabinsa shugaban kasa ta bakin mataimaki na musamman wajen yada labarai da hulda da jamaa, Garba shehu, yace wannnan nasara zata sanyaya ruhin yan kasar.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakintaMajalisar Dokokin Jihar Legas da ke kudancin Najeriya ta sake zaɓar Mudashiru Obasa a matsayin kakakinta bayan Mojisola Meranda ta yi murabus. Matakin na zuwa ne bayan makonnin da aka shafe ana rikici kan shugabancin majalisar, wanda aka fara bayan tsige Obasa tare da maye gurbinsa da Meranda. Bayan murabus ɗin nata, nan take ‘yanmajalisar… Read more: Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a AbujaRahotanni na cewa an yi garkuwa da wani ɗansanda mai suna Modestus Ojiebe wanda ke aiki da rundunar ƴansandan jihar Kwara, a babban titin Kubwa da ke cikin birnin. Jaridar Daily Trust ta ruwaito daga masanin harkokin ƴanbindinga, Zagazola Makama da ma wasu majiyoyi daga cikin ƴansandan cewa lamarin ya auku ne a kusa da… Read more: An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.225 ga dalibai 890 da ke karatu a makarantar Tulip International College (NTIC), Mamudo. Za a cigaba da biyan wannan tallafi har tsawon shekaru shida, tun daga matakin karamar sakandire har zuwa ajin karshe na babbar sanadire. A yayin bikin kaddamar da… Read more: Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin NajeriyaKungiyar Dalibai ta kasa (NANS) ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin kasa idan gwamnonin jihohin Bauchi, Katsina, Kano, da Kebbi ba su janye shawarar rufe makarantu na tsawon makonni biyar domin azumin Ramadan cikin sa’o’i 72 ba. A wata sanarwa da mai magana da yawun kungiyar na kasa, Samson Adeyemi, ya fitar a yau,… Read more: Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman maganiKotun Daukaka Kara da ke zamanta a Legas ta yi watsi da bukatar Babban Lauyan Najeriya, Femi Falana, na hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani. Mai shari’a Polycarp Terna Kwahar, wanda ya karanto hukuncin a madadin kwamitin alkalan uku, ya bayyana matsayar kotun. Sauran alkalan, Mai shari’a Mohammed Mustapha da Mai shari’a… Read more: Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
- Ƙungiyar dattawan arewa ta nemi a yi bincike kan rikicin Natasha da AkpabioƘungiyar dattawan arewacin Najeriya, wato Arewa Consultative Forum ko kuma ACF a taƙaice ta nuna damuwarta kan zargin cin zarafi da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi ga shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio. A wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi wanda kakakin ƙungiyar, Muhammad-Baba ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta ce akwai buƙatar… Read more: Ƙungiyar dattawan arewa ta nemi a yi bincike kan rikicin Natasha da Akpabio
Haka kuma Ya yabawa maza da mata da suka bada gudummawa a fannin lafiya, wanda ya alakanta nasarar da jajircewarsu da goyon bayansu wajen kawo karshen jinyar.
Buhari yace wannan nasara ba ita kadai alummar kasar suka cimmaba a lokacin mulkinsa, kuma wannan abune da baza a taba mantawa dashiba a idan aka tina mulkinsa, wannan nasara ta kawo daidaito wajen ciyar da kasar gaba a fannin lafiya tun a shekarar 2015.