Hukumar WHO za ta samar da magunguna kyauta ga yara masu fama da cutar sankara

0 35

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, ta sanar da kaddamar da wani sabon shiri da zai samar da magunguna kyauta ga dubban yara masu fama da cutar sankara a kasashe masu matsakaicin karfi da marasa karfi.

A cewar hukumar, kasashen Mongoliya da Uzbekistan sun fara karɓar magungunan, tare da shirin isar da su zuwa Ekwado, Urdun, Nepal da Zambiya a matakin gwaji.

Wannan shiri zai amfani akalla yara 5,000 a bana, tare da fatan kaiwa kasashe 50 cikin shekaru biyar zuwa bakwai.

WHO ta ce mafi yawan yara a kasashe masu karancin tattalin arziki na rasa ransu sakamakon rashin magani mai inganci da katsewar jinya.

Leave a Reply