Hatsarin mota yayi sanadiyyar mutuwar mutum 10 a Legas

0 20

Mutum 10 ciki har da ƙananan yara uku da manya bakwai ne suke rasa rayukansu a wani hatsarin mota a yankin Abule Osun da ke babban titin Lagos-Badagry da ke jihar Legas a daren Talata.

Wata sanarwa da babban sakatare na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa na jihar Legas, Olufemi Oke-Osanyintolu ya fitar, wanda tashar talabijin ta Channels ta ruwaito, ya ƙara da cewa wasu mutum uku sun jikkata.

Hatsarin ya auku ne bayan wata mota ƙirar Siena ta haɗu da wata babbar mota da ke ajiye.

Oke-Osanyintolu ya ce binciken da suka gudanar ya nuna cewa motar ta Siena tana gudun wuce ƙima ne, inda ta buga da motar da ke tsaye ba tare da ya lura ba.

  • BBC

Leave a Reply

%d bloggers like this: