Gwamnonin Arewa sun ɗaura ɗamarar yaƙi da matsalar rashin abinci mai gina jiki a yankin

0 152

Gwamnonin Arewa sun ɗaura ɗamarar haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya da sauran masu ruwa da tsaki domin yaƙi da matsalar rashin abinci mai gina jiki a yankin. Gwamnonin sun ƙuduri wannan aniyar ce yayin wani taron tattaunawa kan ƙarancin abinci mai gina jiki mai taken Karuwar Rashin Abinci Mai Gina Jiki a Arewa, Magance Matsalar Da Ta Tunkaro. Cibiyar tsare-tsare da gudanar da mulki ta Athena tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Lafiya da Walwalar Jama’a ta Tarayya ne suka shirya taron wanda ya gudana a Otel ɗin Transcorp da ke Abuja.

Leave a Reply

%d bloggers like this: