Ministan ayyuka, Babatunde Fashola, ya sanar da haka lokacin da yake gabatar da tsare-tsaren shirin ga hadakar kwamitocin ayyuka na majalisun kasa.
Ministan yace masu zuba jari zasu gudanar da aiki da kula da manyan titunan.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
- Ƙungiyar dattawan arewa ta nemi a yi bincike kan rikicin Natasha da Akpabio
Fashola yace Zangon farko na aiki zai lakume kudi naira biliyan 163 da miliyan 320, akan kimanin naira biliyan 16 domin kowane titi guda daga cikin goman.
Titunan sune na Benin zuwa Asaba, Abuja zuwa Lokoja, da Kaduna
zuwa Kano, da Onitsa zuwa Owerri zuwa Aba, da Shagamu zuwa Benin, da Abuja zuwa
Keffi zuwa Akwanga, da Kano zuwa Maiduguri, da Lokoja zuwa Benin, da Enugu zuwa
Fatakwal da kuma Ilorin zuwa Jebba.