Gwamnan Jihar Zamfara Ya Mayar Wa Alhaji Aliyu Garba Marafa Sarautarsa Ta Sarkin Birnin Yandoto

0 146

Gwamnan jihar Zamfara Muhammed Bello Matawalle, ya mayar wa Alhaji Aliyu Garba Marafa sarautarsa ta sarkin Birnin Yandoto.

Kafin hakan dai a watan Yulin shekarar da ta gabata ne gwamnan ya dakatar da sarkin saboda ya bai wa jagoran ‘yan bindiga Ado Aleiru sarautar sarkin Fulani a fadarsa.

Naɗin dai, ya janyo ce-ce-ku-ce a ciki da wajen jihar.

A cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Kabiru Balarabe Sardauna ya fitar, ta tabbatar da mayar da sarkin kan karagarsa.

Sanarwar ta ce an mayar da sarkin ne sakamakon buƙatar hakan daga kwamitin da gwamnati ta kafa domin bincike kan lamarin.

Tun da farko dai sarki ya ce ya bai wa Ado Aleiru sarautar ne sakamakon rawar da ya taka wajen wanzar da zaman lafiya tsakanin masarautar da ‘yan bindigar da ke addabar ƙaramar hukumar Tsafe. Sanarwar ta kara da cewa bayan bincikar sarkin, kwamitin bai same shi da wata alaka da Ado Aleiru ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: