Shugaban Karamar Hukumar, Hudu Babangida Dambazau wanda ya bayyana haka ga manema labarai a garin Gantsa, ya ce garuruwan da ambaliyar tafi kamari sune, Gantsa da Shawu da Buji da Matikir da Tsamfau da kuma Kukuma.
Babangida Dambazau wanda ya sami wakilcin mataimakin sa, Ahmed Zubairu, ya ce kayayyakin amfanin gona da suka lalace sun hadar da gero da dawa da wake da rogo da kuma shinkafa.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Ya kara da cewa ambaliyar ta lalata hanyar da ta tashi daga Gantsa zuwa Tsamfau.
A jawabin sa, mai magana da yawun al’ummomin da ambaliyar ta shafa, Nazifi Garba ya roki gwamnatin tarayya da ta jiha da kuma ta karamar hukuma da sauran masu hannu da shuni su kai musu daukin gaggawa.