Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya saki fursunoni 293 wanda suke tsare a gidajen gyaran Da’a a jihar ta Kano.
Sakin nasu yazo ne bayan umarnin da gwamnatin tarayya ta bawa Jihohi, kan su rage Cunkoso a gidajen gyaran da’ar, saboda annobar Coronavirus.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Mai magana da yawun Rundunar hukumar Gyaran Da’ar na Jihar Kano DSC Musbahu Lawan Nassarawa, shine ya tabbatar da sakin Fursunonin cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai.

DSC Lawan, ya bayyana cewa gwamnan Jihar ta Kano ya biya kudi kimanin Naira Miliyan 12 ga Fursunonin tare da basu naira dubu 5 domin suyi kudin Mota zuwa gida.
Kazalika ya bukaci Fursunonin da aka saka su kasance masu canza halaiyar su, saboda damar da aka basu na zama mutanen kirki.