Gwamnatin tarayya ta amince da dawo da jigilar jiragen sama a cikin kasa da zarar komai ya daidaita, bisa tanadin ka’idojin kariya daga cutar corona na cikin gida da na kasa da kasa.
Shugaban kwamitin karta kwana na shugaban kasa kan cutar corona, Boss Mustapha, ya sanar da haka wajen taron manema labarai na kwamitin a Abuja.
Yace dawowa jigilar jiragen zata zo da karin kudin tikitin jirgin sama.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Yayi bayanin cewa karin kudin kayayyaki da na ayyuka, ba bangaren sufurin jiragen sama kadai ya shafa ba.
A cewarsa, farashin abubuwa sun yi tashin gwauron zabi tun bayan barkewar annobar.
An rufe filayen jiragen sama a Najeriya a watan Maris, lokacin da kasar ta fara kokarin dakile bazuwar cutar corona, wacce tayi silar mutuwar sama da mutane 500 a kasarnan.