Bayan kwashe shekaru yana aikin koyarwa a Jami’ar Bayero dake Kano, babban limamin masallacin birnin tarayya dake Abuja Farfesa Ibrahim Ahmad Said Maqariy (Hafizahulla) ya ajiye aikinsa domin maida hankali wajen hidimtawa Addini.
Bayan Jami’ar ta Bayero ta amince da ajiye aikin malamin, a wata takarda dake dauke da amincewar hukumar makarantar.
Malam Maqarin ya bayyana cewa ya dauki wannan matakin ne domin yana daya daga cikin mafarkinsa tun bai wuce Shekara Ashirin ba,yake fatan ya daina aikin gwamnati.
- Akwai yiwuwar jefa ƴan Najeriya cikin duhu matuƙar gwamnati bata biya bashin Naira Triliyan huɗu ba
- An raba Naira Triliyan 1.57 a tsakanin gwamnatocin tarayya, jihohi da kananan hakumomi a Najeriya – FAAC
- Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kara filayen noman shinkafa zuwa hekta 500,000 nan da shekarar 2030
- Gwamnomin Jam’iyyar PDP sunyi watsi da shirin yin kawance domin kawar jam’iyyar APC
- Ƴan Nijar mazauna Libya sun buƙaci gwamnatin Nijar ta kai musu ɗauki
Sai a wannan Shekarun Allah Ya karbeshi a matsayin Mai cikakken yiwa addini hidima da Ma’aikatan Addini.
Inda ya kara da cewa Koda yake kowa da yanda Allah Ya tsara masa rayuwarsa, ba ya nufin wadanda ba haka ba ya fisu.
Maqari “Alhamdulillah da na bar Aikin Albashi da Kaina da Qarfina. Allah Ya Albarkaci abinda zai biyo baya na”