Tsohon shugaban kasa Olusegun Obansanjo yayi kira ga matasan Afirka da su kawar da dattawa daga shugabanci.
Obasanjo ya bukaci matasan da su tsunduma a harkokin jam’iyyun siyasa domin kwace madafun iko daga hannunsu.
Tsohon shugaban kasar ya fadi haka a jiya lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen wata tattaunawa ta bidiyon kai tsaye, domin tunawa da ranar matasa ta duniya ta bana.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Cibiyar cigaban matasa, wacce bangare ne na dakin karatun shugaban kasa na Olusegen Obansanjo dake Abekutan jihar Ogun, ta shirya tattaunawar.
An zabo mahalarta daga Najeriya da Mali da Amurka da Ghana da Kenya da Afirka ta Kudu.
A cewarsa, muddin ba dattawa aka kora daga siyasa ba, zasu cigaba da rike mukamai, suna barin matasa a iska.