Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa a ofishin mataimakin shugaban ƙasa, Dokta Hakeem Baba-Ahmed ya ajiye aikinsa.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa tsohon kakakin na ƙungiyar dattawan arewa ya ajiye aikin ne kimanin mako biyu da suka gabata.
Sai dai bai bayyana daliinsa na ajiye aikin, inda da ya ce kawai ya ajiye aikin ne saboda wasu dalilai nasa.
A watan Satumban shekarar 2023 ne shugaban Najeriya Bola Tinubu na naɗa Hakeem a matsayin mai ba shi shawara kan harkokin siyasa a ofishin mataimakin shugaban ƙasa.
Ƴan arewa musamman matasa a kafofin sadarwa suna yawan caccakar Hakeem Baba-Ahmed a duk lokacin da aka yi wani abu da suke gani ba a kyautawa arewa ba, musamman saboda tsohon muƙaminsa, inda yake yawan fitowa yana magana a kan abubuwan da suka shafi yankin.