Gwamna Nasiru El-Rufa’i na jihar Kaduna yace bangaren shari’a a jihar bazai sake bayar da belin masu fyade ba, daidai lokacin da ake duba yiwuwar dandake wadanda aka yankewa hukuncin fyade.
El-Rufa’i ya sanar da haka lokacin da wata tawagar mata da ke neman adalchi ga wadanda ake yiwa fyade, ta shirya wata zanga-zangar lumana a gidan gwamnati dake Kaduna a jiya.
Yace alkalin alakai na jihar ya bayar da tabbacin cewa daga yanzu baza a sake bayar da belin duk wanda aka zarga da aikata fyade ba, ta kowane hali, kasancewar suna komawa su sake aikata laifin.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
A cewarsa, tuni jihar take da tsatstsauran hukunci akan laifin aikata fyade.
Sai dai, El-Rufa’i yace gwamnati na duba yiwuwar gyaran dokar domin sanya dandaka ga duk wanda aka zartarwa da hukuncin fyade.
A cewarsa, tuni wani dan majalisar dokokin jihar ya shirya gabatar da kudiri akan sanya dandaka.