Gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ta amince da kafa wata sabuwar hukuma da zata yaki cin hanci da rashawa.
Sabuwar hukumar wacce majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da ita, za a dora mata nauyin kula da dukkan kadarorin satar da aka kwato.
Ministan shari’ah kuma babban lauyan tarayya, Abubakar Malami, ya sanar da haka ga manema labaran fadar shugaban kasa, bayan zaman ganawar majalisar zartarwa ta tarayya wanda aka gudanar a jiya laraba.
- Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kara filayen noman shinkafa zuwa hekta 500,000 nan da shekarar 2030
- Gwamnomin Jam’iyyar PDP sunyi watsi da shirin yin kawance domin kawar jam’iyyar APC
- Ƴan Nijar mazauna Libya sun buƙaci gwamnatin Nijar ta kai musu ɗauki
- Za a kammala sabunta titin Abuja-Kaduna-Kano cikin wata 14 – Ministan ayyuka
- Gwamnatin Najeriya ta kafa kwamiti don nazarin tasirin sabon harajin Amurka
Yace sabuwar hukumar za ta sake bibiyar yadda ake kula da kadarori da dukiyoyin da aka kwato daga hannun marasa gaskiya.
Ministan yace majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da aikawa da kudirin neman kafa hukumar zuwa ga majalisar kasa.