Shugaban Sojojin Kasa, Laftanal Janar Tukur Burutai yayi gargadin cewa sojoji baza su kyale bata gari su tarwatsa zaman lafiyar Najeriya ba.
Mukaddashin daraktan hulda da jama’a na hukumar soji, Kanal Sagir Musa, yace Buratai ya fadi hakan a jiya yayin zaman ganawa da manyan jami’an soji da kwamandojin barikoki da na filin yaki, wanda aka gudanar a Abuja.
Sagir Musa ya yiwa yan jarida jawabi akan abin da aka tattauna a zaman ganawar, lokacin da yake zantawa da manema labarai.

Tukur Buratai ya gayawa manyan jami’an soji da kwamandojin barikoki da na filin yaki cewa babu hurumin rashin biyayya tsakankanin dukkan jami’ai da sojojin Najeriya.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Ya bayar da umarnin cewa dole su jaddadawa na kasa da su cewa hukumar soji ta jajirce wajen tabbatar da dorewar mulkin demokradiyya a Najeriya, kasancewar ita ce hanya daya tilo wajen samar da cigaba.