An umarci kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja da ya biya wasu al’ummomi diyya

0 105

Hukumar da ke sa ido kan wutar lantarki ta kasa ta umarci kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja da ya biya diyya ga wasu al’ummomi a Kogi da Abuja sakamakon rashin aikin yi.

A cewar takardar da  hukumar ta fitar a ranar Alhamis, yankunan da lamarin ya shafa sun hada da Wuse, Garki, Asokoro, da kuma Ajaokuta a Lokoja, jihar Kogi.

Wadannan yankunan sun fuskanci karancin wutar lantarki tsakanin 1 zuwa 25 ga Agusta, 2024, duk da cewa suna kan Band A.

A cewar hukumar, duk wani mai amfani da wutar da ya kasa cika sa’o’in da ake bukata na tsawon kwanaki bakwai a jere, za a rage masa kudin wutar, kuma dole ne a biya  shi diyya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: