Sashen bada horo da jagoranci dake ofishin shugaban ma’aikata na jihar Jigawa yace a gobe Asabar 10 ga wata ne za a kai matasan jihar Jigawa zuwa makarantar horas da kananan hafsoshin soji ta NDA dake Kaduna domin ganawa dasu.
- An kwaso ‘yan Najeriya 144 da suka maƙale a Libya zuwa gida
- Akalla likitoci 16,000 ne suka fice daga Najeriya cikin shekara 6 – Pate
- Rashin daidaito a nade-naden mukamai na kawo cikas ga hadin kan Nijeriya – Sanata Ndume
- Najeriya ba ta cikin ƙasashen da Saudiyya ta daina bai wa biza – Gwamnatin Najeriya
- Nuhu Ribadu ya kawo ziyarar ta’aziyya ga Gwamnan Jigawa a gidan gwamnati da ke Dutse
A sanarwar da Daraktan sashen Ibrahim Abdullahi ya bayar ta bukaci matasan da za a gana da su da su hallara a ofishin hukumar bada guraben karatu ta jiha dake Dutse da misalin karfe 7 na safe domin dibarsu zuwa Kaduna.
Sanarwar ta bukaci matasan da abin ya shafa da su kiyaye da wannan sanarwa kuma su zo akan lokaci.