Rundunar yansandan jihar Jigawa ta kame mutane 20 da take zargi da aikata laifuka daban-daban da suka hada da fashi da makami, garkuwa da mutane da kisan kai, inda ta kwato kayan sata daga hannunsu da kuma makamai.
Kwamishinan yansanda na jiha, Usman Sule Gomna, ya sanar da haka a taron manema labarai a Dutse.
Kwamishinan ya bayyana cewa tawagar yansanda ta musamman masu yaki da fashi da makami sun kai farmaki kan wasu maboyar ‘yan fashi a yankin karamar hukumar Ringim inda suka damke wasu daga cikin ‘yan fashin.
- Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kara filayen noman shinkafa zuwa hekta 500,000 nan da shekarar 2030
- Gwamnomin Jam’iyyar PDP sunyi watsi da shirin yin kawance domin kawar jam’iyyar APC
- Ƴan Nijar mazauna Libya sun buƙaci gwamnatin Nijar ta kai musu ɗauki
- Za a kammala sabunta titin Abuja-Kaduna-Kano cikin wata 14 – Ministan ayyuka
- Gwamnatin Najeriya ta kafa kwamiti don nazarin tasirin sabon harajin Amurka
Ya kara da cewa jami’an yansanda a karamar hukumar Babura sunyi arangama da wasu yan bindiga 9 a kauyen Andau dake yankin karamar hukumar.
Sule Gomna ya kuma ce tawagar yansanda ta musamman masu yaki da fashi da makami sun kama mutane 10 da ake zargin barayine yan bindiga a kwaryar birnin Dutse.