‘Yan Najeriya 1,500 Da Aka Kwaso Daga Kasar Sudan Za Su Isa Abuja A Yau

Gwamnatin tarayya ta ce rukunin farko na ‘yan Najeriya da aka kwaso daga kasar Sudan mai fama da rikici za su iso Abuja a yau.

Shugabar hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa ce ta bayyana hakan ga manema labarai jiya a Abuja.

Ta ce sama da ‘yan Najeriya miliyan uku ne ke zaune a kasar Sudan kuma ana kokarin kwashe mutane da dama idan har yakin ya ci gaba, ta kara da cewa za a bayar da fifiko ga yara da dalibai da mata.

Da take magana jiya a wani shirin gidan Talabijin na Channels, Dabiri-Erewa, ta ce jami’o’in Najeriya sun yi tayin karbar daliban Najeriya da suka dawo daga Sudan.

Direbobi kashin farko na bas biyar da ke jigilar daliban Najeriya da suka bar birnin Khartoum a ranar Laraba sun yi watsi da su a cikin jeji na tsawon sa’o’i sabo da rashin biyansu kudi. Sai dai hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA) ta ce an shawo kan dukkan matsalolin.

Comments (0)
Add Comment