Hukumar samar da ayyukan yi ta kasa ta fara bayar da horo ga matasa dubu 1 da 350 a jihar Jigawa.
Jagoran hukumar na jiharnan, Malam Abubakar Jamo, ya sanar da haka a wata ganawa da kamfanin dillancin labarai na kasa a Dutse.
Abubakar Jamo yace aikin horon na watanni 3 wanda aka fara a wannan watan na Oktoba, za a gudanar da shi a karkashin shirin hukumar na koyar da sana’o’in hannu.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Yayi bayanin cewa an zabo mutane 50-50 daga kowace karamar hukuma cikin kananan hukumomin jiharnan 27 domin cin gajiyar shirin.
Abubakar Jamo ya kara cewa za a bayar da horo akan gyaran mota da dinki da gyaran injinan wuta da aikin komfuta da kafinta da gyaran wayar hannu da aikin jima da aski da kuma zane-zane.
Jagoran yayi nuni da cewa za a bayar da horon ne da nufin rage zaman kashe wando tsakankanin matasa a jiharnan.