Hukumar yan sanda ta kasa ta zata hada hannu da kwamatin kasa da kasa na hukumar agaji ta Red Cross da sauran hukumomin cigaba, wajen bayar da horo ga sabuwar rundunar SWAT da ta maye gurbin rundunar yan sanda ta musamman dake yaki da ayyukan fashi da makami wato SARS.
Kusan jami’ai 1,850 ne ake sa ran zasu halarci shirin bayar da horon na tsawon makonni 3, wanda za’a gudanar a makarantar baiwa yan sanda horo dake Ila Oragun a jihar Osun, da kuma ta Ende Hills dake jihar Nassarawa.
Kakakin hukumar Frank Mba, yace jami’an sabuwar rundunar ta SWAT, zasu karbi horo ne kan dokokin kiyaye dan adam da hakkokinsa, makamar jami’in dan sanda a halin rikici, kamawa da kuma tsare mai laifi da dai makamantansu.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Masu gudanar da shirin bada horon sun hadar da jami’ai daga hukumomin cigaba, kwararru a fannin tsaro da kuma yan fafutuka daga kungiyoyn fararen hula.