Ofishin hukumar hana safarar mutane ta kasa na shiyyar Kano ya kama wasu mutane uku a Kano bisa zargin sayar da wani yaro dan shekara daya a jihar Imo.
Wadanda ake zargin sune kwamandan Hisbah na Fagge, Jamilu Mohammed, da dagacin Fagge, tare da wata mata mai suna Loveth wacce ta sayi yaron.
Shugaban ofishin shiyyar, Shehu Umar, ya gayawa manema labarai cewa an gayyaci wadanda ake zargin domin amsa tambayoyi dangane da lamarin.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
An gano cewa yaron da aka sayar, iyayensa ne suka jefar da shi, kuma ake kula da shi a hukumar Hisbah.
Sai dai, an zargin kwamandan Hisbah ya hada baki da dagacin inda suka sayar da shi. A cewar shugaban hukumar, yaron wanda ake zargin kwamandan Hisbah tare da dagacin Fagge sun sayar da shi ga Loveth, an ceto shi daga hannun mahaifiyar Loveth a jihar Imo.