Saɓa dokokin Majalisar Dattawa ne yasa muka dakatar da Sanata Natasha –

Majalisar Dattawan Najeriya ta ce ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ne saboda saɓa dokokin majalisar da ta yi, ba don zargin cin zarafin da ta yi wa shugaban majalaisar ba.

Cikin wata sanarwa da shugaban masu rinjaye na majalisar, Sanata Bamidele Opeyemi ya fitar ranar Asabar a madadin majalisar, ya ce dakatar da Sanatar, mataki ne da duka majalisar ta ɗauka, saboda saɓa dokokinta da Sanata Natasha ta yi.

”An dakatar da ita ne saboda yadda take keta dokoki da ƙa’idojin majalisa, da nuna rashin ɗa’a a majalisar, wannan shi ne laifinta babu daɗi babu ragi.” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sanarwar ta ce inda ƴarmajalisar ta yi aiki da dokoki da ƙa’idojin majalisar, da majalisar za ta karɓi ƙorafinta, kamar yadda doka ta tanada, ”amma ba ta bi ƙa’ida da dokokin da suka kafa majalisar da take aiki a cikinta ba”.

Sanata Bamidele ya ce majalisar ta ɗauki matakin dakatar da ƴarmajalisar ne bisa shawarar kwamitin ɗa’a, wanda ya sameta da laifin saɓa wa sashe na 6.1 da sashe na 6.2 na dokokin majalisar, sannan ya bayar da shawarar dakatar da ita.

Sanarwar ta kuma zayyano wasu laifuka biyar da ta ce Sanata Natasha ta aikata, ciki har da ƙin zama a kujerar da aka sauya mata a lokacin zaman majalisar na ranar 25 ga watan Fabrairu, da yin magana ba tare da amincewar jagoran zaman majalisar ba, da yin kalaman zagi da rashin girmamawa da shugabancin majalisar.

Comments (0)
Add Comment