Kungiyyar cigaban masarautar Hadejia (HEDA) ta dora alhakin ambaliyyar ruwan da ke faruwa akan gwamnatocin yanzu da na baya na tarayya da jiha.
Masarautar dake yankin arewa maso gabas na jihar Jigawa, tana da kananan hukumomi 8 a karkashinta, wadanda suka hada da Hadejia, Kaugama, Auyo, Malammadori, Birniwa, Guri, Kirikasamma and Kafin Hausa.
Shugaban kungiyyar , Abdullah Sarki Kafinta, wanda ya zanta da manema labarai anan cikin garin Hadejia, ya bayyana takaicin sa kan yadda al’ummar cikin garin Hadejia suka rasa kadarorinsu, gidaje da rayukansu sanadiyyar ambaliyyar ruwan.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Sannan yayi kira ga gwamnatin tarayya da taimakawa al’ummar yankin da irin shuka daban daban da irin kifi daza a zuba a kududdufai idan ambaliyyar ruwan ta wuce.