Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a 12 ga watan Yuni a matsayin ranar hutun ranar demokradiyya ta bana.
Ministan cikin gida, Rauf Aregbesola, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa a madadin gwamnatin tarayya.
Sanarwar wacce ke dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Georgina Ehuriah, ta jiyo Aregbesola na taya ‘yan Najeriya murnar dorewar mulkin demokradiyya a kasarnan.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Ministan ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su cigaba da godewa kokarin da aka yi wajen dawo da mulkin demokradiyya.
Ya tabbatarwa da ‘yan Najeriya jajircewar gwamnatin tarayya wajen yaki da annobar corona tare da hadin kan dukkan ‘yan Najeriya.