Sarkin Kano, Mai Martaba Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yabawa gwamna Muhammadu Badaru Abubakar bisa aiwatar da ayyukan raya kasa a jihar Jigawa.
Ya sanar da haka lokacin da ya kaiwa gwamnan ziyara a gidan gwamnatin dake Dutse.
Sarkin ya bayyana cewa yayin ziyararsa zuwa masarautun jiharnan, ya yaba da ayyukan da suka kawata birane da yankunan karkara a fadin jihar.
- Gwamnatin Najeriya ta kafa kwamiti don nazarin tasirin sabon harajin Amurka
- Jam’iyyun adawa ba zasu iya haɗa kansu don tunkarar APC a zaɓen shekarar 2027 ba – Bukola Saraki
- Dakarun Operation Delta Safe sun rusa haramtattun matatun mai guda 22 a cikin makon da ya gabata
- “Jam’iyyun hamayya na son ƙulla wata haɗaka da ba za ta yi tasiri ba” – Ganduje
- Jihohi 18 na Arewacin Najeriya za su fuskanci matsanancin zafi – NiMet
- Najeriya ta sake kiran da a sako Bazoum da matarsa
Aminu Ado Bayero ya gayawa gwamnan cewa yazo jihar ne domin gabatar da kansa tare da neman shawarwarin sarakunan, inda ya godewa mutanen jiharnan bisa kyakykyawar tarbar da suka yi masa.
Da yake mayar da martani, Gwamna Badaru Abubakar yace yayi farinciki da alfahari da ziyarar sarkin, wacce yace zata karfafa danganta mai kyau da tarihi tsakanin mutanen jihoshin Kano da Jigawa.