Hukumar samarda aiyukan yi ta kasa NDE ta kaddamar da bada horan watanni uku ga matasa maza da maza guda dari a jihar Jigawa.
Shugaban hukumar a jihar nan Malam Abubakar Jamo ya sanar da hakan a lokacin ganawa da manema labarai a garin Dutse.
Yace wasu daga cikin matasan zasu sami horo akan bangarori daban daban na aikin gona.
- Gwamnatin Najeriya ta kafa kwamiti don nazarin tasirin sabon harajin Amurka
- Jam’iyyun adawa ba zasu iya haɗa kansu don tunkarar APC a zaɓen shekarar 2027 ba – Bukola Saraki
- Dakarun Operation Delta Safe sun rusa haramtattun matatun mai guda 22 a cikin makon da ya gabata
- “Jam’iyyun hamayya na son ƙulla wata haɗaka da ba za ta yi tasiri ba” – Ganduje
- Jihohi 18 na Arewacin Najeriya za su fuskanci matsanancin zafi – NiMet
Mallam Jamo ya kara da cewar ana gudanar da bada horan ne karkashin shirin bada horo a yankunan karkara.
Inda yace matasan za a tura su wuraren koyan sanin makamar aiki na makonni biyu a gonaki.
Mallam Abubakar Jamo ya shawarci matasa dasu shiga cikin shirin domin samun hanyoyin dogaro da kai.