Masarautar jihar Katsina, tabi sahun takwarorinta na Kano da nan Jigawa, biyo bayan daukar matakin soke gudanar da shagulgulan bikin sallah babba dake tafe.
Masarautar dai ta aikewa da gwamnatin jihar, dangane da matakin, wanda ta bayyana matsalar tsaro, hadi da cutar alakakai ta corona, a matsayin musabbabi.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Wasikar wadda aka rubuta da yaren Hausa, aka kuma aikewa da sakataren gwamnatin jihar Alhaji Inuwa Mohammad, na dauke ne da sa hannun sakataren masarautar kuma sallaman Katsina Alhaji Mamman Ifo.
Cikin wasikar, masarautar ta bukaci al’umma da gudanar da bukukuwan sallarsu daga gida, tare da rokon su da suyi amfani da lokacin, wajen yiwa jihar dama kasa baki daya Addua.