Masarautar jihar Katsina, tabi sahun takwarorinta na Kano da nan Jigawa, biyo bayan daukar matakin soke gudanar da shagulgulan bikin sallah babba dake tafe.
Masarautar dai ta aikewa da gwamnatin jihar, dangane da matakin, wanda ta bayyana matsalar tsaro, hadi da cutar alakakai ta corona, a matsayin musabbabi.
- Gwamnatin Najeriya ta kafa kwamiti don nazarin tasirin sabon harajin Amurka
- Jam’iyyun adawa ba zasu iya haɗa kansu don tunkarar APC a zaɓen shekarar 2027 ba – Bukola Saraki
- Dakarun Operation Delta Safe sun rusa haramtattun matatun mai guda 22 a cikin makon da ya gabata
- “Jam’iyyun hamayya na son ƙulla wata haɗaka da ba za ta yi tasiri ba” – Ganduje
- Jihohi 18 na Arewacin Najeriya za su fuskanci matsanancin zafi – NiMet
Wasikar wadda aka rubuta da yaren Hausa, aka kuma aikewa da sakataren gwamnatin jihar Alhaji Inuwa Mohammad, na dauke ne da sa hannun sakataren masarautar kuma sallaman Katsina Alhaji Mamman Ifo.
Cikin wasikar, masarautar ta bukaci al’umma da gudanar da bukukuwan sallarsu daga gida, tare da rokon su da suyi amfani da lokacin, wajen yiwa jihar dama kasa baki daya Addua.