Majalisar wakilai ta kasa ta soki batun jinginar da yancin kan kasa a yarjejeniyar bashin Najeriya da China, inda tace abune mai hadari sosai.
Shugaban kwamitin yarjejeniyoyi na majalisar, Nicholas Ossai, wanda ya sanar da haka a Abuja, a wajen taron jin bahasin basussukan kasashen waje, yace yarjejeniyar bashin Najeriya da kasar China, tana aiki ne da dokokin kasar China.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Yace duk da kasancewar gwanatin tarayya a shekarar 2014, ta sanya hannu akan dokar majalisar zartarwa wacce ta samar da ka’idoji akan jinginar da yancin kan kasa lokacin tattaunawar yarjejeniyar, jami’an gwamnatin tarayya na taka dokar.
Mambobin majalisar zartarwa wadanda suka bayyana a gaban kwamitin sun hada da Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, da Ministan Ayyuka da Gidaje, Babatunde Fashola, da ministan Sadarwa, Isah Ali Pantami, da ministan harkokin yansanda, Muhammad Maigari, da ministan babban birnin tarayya, Mohammed Bello, da sauransu.