Kwamishinan kasuwanci da masana’antu na jihar Bauchi, Mohammed Sadiq, yayi murabus daga mukaminsa.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Kwamishinan a sanarwar tasa, ya godewa tsohon kakakin majalisar wakilai ta kasa, Yakubu Dogara, wanda a cewarsa shine yayi silar bashi mukamin.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Hadimin Yakubu Dogara mai yada labarai, Turaki Hassan, shima ya yada sanarwar ta sa.
Wata daya baya, Yakubu Dogara, ya fice daga jam’iyyar PDP, inda ya koma tsohuwar jam’iyyarsa ta APC.
Ficewar tasa daga jam’iyyar tazo ne bayan rikici tsakaninsa da gwamnan jihar, Bala Mohammed.