Kungiyoyin Kwadago sun yi tir da ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas

Kungiyar Kwadago ta kasa, NLC, da Kungiyar ‘Yan Kasuwa ta TUC sun yi tir da ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas tare da dakatar da zababbun shugabannin jihar da shugaba Tinubu ya yi.

Kungiyoyin sun bayyana matakin Shugaban kasar a matsayin take doka, suna masu cewa hakan ya saba wa Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin kasar na 1999.

Sun bukaci a janye wannan mataki nan take domin kare dimokuradiyya da kwanciyar hankalin ma’aikata da tattalin arzikin kasar nan.

A wata sanarwa kan wannan batu da shugabannin NLC da TUC suka fitar, sun gargadi gwamnati da kada ta mayar da Najeriya kasar da ake wulakanta dokokin mulkin dimokuradiyya.  

Comments (0)
Add Comment