Majalissar zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da fitar da kudi sama da naira miliyan 194 domin gudanar da karin ayyukan magance zaizayar kasa da ambaliyar ruwa a wajen da ake gina sabon asibitin kwararru na Kazaure.
Kwamishinan yada labarai matasa da wasanni na jiha Alhaji Bala Ibrahim Mamsa ya sanar da hakan bayan zaman majalisar da Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ya jagoranta.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Ibrahim Mamsa yayi bayanin cewa majalisar ta amince da karin ayyukan ne sakamakon rahotan data samu wanda ke nuni da cewar zaizayar kasa da ambaliyar ruwa na barazana ga aikin gina asibitin.
Kwamishinan ya cigaba da cewa tun farko an bada kwangilar aikin ne akan kudi naira biliyan dubu 1 da miliyan 893.