Asusun kiwon lafiya na jihar Jigawa yace kawo yanzu asibitoci masu zaman kansu guda 10 ne suka nuna sha’awarsu ta shiga shirin asusun adashen gata na kiwon lafiya na jiha.
Sakataren zartarwa na asusun Dr Nura Ibrahim ya sanar da haka ga Radio Jigawa.
Yace daga cikin asibitocin masu zaman kansu da suka yi rijistar shiga shirin sun hadar da guda uku a garin Hadejia da daya a Dutse da daya a Ringim da uku a Kazaure da kuma daya a Maigatari da daya a Babura.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Dr. Nura Ibrahim yace kawo yanzu sun shigar da ma’aikatan jiha da kananan hukumomi da na sashen ilmi dubu 25 da 116 ne aka yiwa rijista kawo yanzu.
Yace a mako mai zuwa jirgin rijistar zai ziyarci kananan hukumomin Mallam Madori da Auyo da Kaugama.