Gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani kwamitin tsakanin ma’aikatu wanda zai lalubo hanyoyin da za abi a rage barnar da ambaliyar ruwa ke jawowa a fadin kasarnan.
Ministar jin kai, kula da annoba da jin dadin jama’a, Sadiya Umar Farouq, wacce ta kaddamar da kwamitin a Abuja, tace kwamitin zai yi aiki tukuru wajen samar da wani shirin kasa na shiryawa annoba da bayar da tallafi.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Ministar tace hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa NEMA ta samar da hanyoyin kula da ambaliyar ruwa, kuma akwai shirin kai ziyara zuwa ga gwamnatocin jihoshi domin duba yadda aka shirya da kuma bayar da agajin ambaliyar ruwa.
Yace an zakulo yan kwamitin daga ma’aikatar jin kai, kula da annoba da jin dadin jama’a, da ma’aikatar da albarkatun ruwa da ma’aikatar gona da ta muhalli da ma’aikatar cikin gida da ta yada labarai, da sauransu.