Gwamnatin Jihar Jigawa ta rabawa manoma 50 ingantaccen irin shuka dan Brazil domin nomawa a gona mai fadin kadada 80 a wannan damina.
Mai bawa Gwamna shawara kan noman shinkafa, Alhaji Jamilu Dan-Mallam ya bayyana haka lokacin da ya jagoranci wata tawaga ta masu ruwa da tsaki a aikin gona zuwa wasu fadamu dake kananan hukumomin Dutse da Hadejia da Kazaure.
- Gwamnatin Najeriya ta kafa kwamiti don nazarin tasirin sabon harajin Amurka
- Jam’iyyun adawa ba zasu iya haɗa kansu don tunkarar APC a zaɓen shekarar 2027 ba – Bukola Saraki
- Dakarun Operation Delta Safe sun rusa haramtattun matatun mai guda 22 a cikin makon da ya gabata
- “Jam’iyyun hamayya na son ƙulla wata haɗaka da ba za ta yi tasiri ba” – Ganduje
- Jihohi 18 na Arewacin Najeriya za su fuskanci matsanancin zafi – NiMet
Alhaji Jamilu Dan-Mallam ya shawarci manoman da aka rabawa irin, da su tabbatar sun cika alkawuran da suka dauka na dawo da rancen iri ko kudaden da aka basu domin wasu manoman su amfana.
A nasa jawabin, mukaddashin Manajan Daraktan hukumar bunkasa aikin gona da raya karkara ta jiha, JARDA, Alhaji Bashir Mu’azu Majiya ya yi kira ga manoman da su rika aiki da shawarwarin malaman gona domin bunkasa nomansu.