Gwamnatin Jihar Jigawa ta rabawa manoma 50 ingantaccen irin shuka dan Brazil domin nomawa a gona mai fadin kadada 80 a wannan damina.
Mai bawa Gwamna shawara kan noman shinkafa, Alhaji Jamilu Dan-Mallam ya bayyana haka lokacin da ya jagoranci wata tawaga ta masu ruwa da tsaki a aikin gona zuwa wasu fadamu dake kananan hukumomin Dutse da Hadejia da Kazaure.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Alhaji Jamilu Dan-Mallam ya shawarci manoman da aka rabawa irin, da su tabbatar sun cika alkawuran da suka dauka na dawo da rancen iri ko kudaden da aka basu domin wasu manoman su amfana.
A nasa jawabin, mukaddashin Manajan Daraktan hukumar bunkasa aikin gona da raya karkara ta jiha, JARDA, Alhaji Bashir Mu’azu Majiya ya yi kira ga manoman da su rika aiki da shawarwarin malaman gona domin bunkasa nomansu.