Masu ruwa da tsakin jam’iyyar APC a jihar Yobe sun bukaci majalisar dokokin jihar da ta tsige gwamna Mai Mala Buni, wanda shi ne shugaban riko na jam’iyyar ta kasa, muddin ya gaza yin murabus.
Sun alakanta bukatar ne da gazawar gwamnan wajen sauke nauyin dake wuyansa, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya tanadar a matsayinsa na gwamna.
- Hukumar Hisbah ta fara kama wanzamai da matasan da ke askin zamani
- Mataimakin gwamnan Kano ya jagoranci tawaga zuwa Edo kan kisan matafiya a Uromi
- Matatar Dangote ta rage farashin man fetur zuwa Naira 865
- Gwamnoni 11 na jam’iyyar PDP sun shigar da Tinubu kara a gaban Kotun Koli
- Gwamnan Jihar Filato yayi Allah wadai da kisan mutane 50 da aka yi a jihar
Masu ruwa da tsakin sun zargin gwamna Buni, da yin shakulatin bangaro da lamurran jihar kacokan, inda yakan ziyarci jihar akalla sau guda cikin tsawon wata 1.
Sun bayyana bukatar ne cikin wata sanarwa da suka fitar bayan wani taro da suka gudanar a Abuja.
Sun ce an zabi Buni ne a matsayin gwamnan jihar ba wai shugaban jam’iyya ba, kuma yasha rantsuwar yin biyayya ga kundin tsarin mulkin kasa, to sai dai a yanzu, yayi watsi da al’umarsa a lokacin da suke bukatarsa.