Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya saki fursunoni 293 wanda suke tsare a gidajen gyaran Da’a a jihar ta Kano.
Sakin nasu yazo ne bayan umarnin da gwamnatin tarayya ta bawa Jihohi, kan su rage Cunkoso a gidajen gyaran da’ar, saboda annobar Coronavirus.
- Za a kammala sabunta titin Abuja-Kaduna-Kano cikin wata 14 – Ministan ayyuka
- Gwamnatin Najeriya ta kafa kwamiti don nazarin tasirin sabon harajin Amurka
- Jam’iyyun adawa ba zasu iya haɗa kansu don tunkarar APC a zaɓen shekarar 2027 ba – Bukola Saraki
- Dakarun Operation Delta Safe sun rusa haramtattun matatun mai guda 22 a cikin makon da ya gabata
- “Jam’iyyun hamayya na son ƙulla wata haɗaka da ba za ta yi tasiri ba” – Ganduje
Mai magana da yawun Rundunar hukumar Gyaran Da’ar na Jihar Kano DSC Musbahu Lawan Nassarawa, shine ya tabbatar da sakin Fursunonin cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai.
DSC Lawan, ya bayyana cewa gwamnan Jihar ta Kano ya biya kudi kimanin Naira Miliyan 12 ga Fursunonin tare da basu naira dubu 5 domin suyi kudin Mota zuwa gida.
Kazalika ya bukaci Fursunonin da aka saka su kasance masu canza halaiyar su, saboda damar da aka basu na zama mutanen kirki.