Faransa zata fara kwashe yan kasar ta daga jamhuriyar Nijar

Ma’aikatar harkokin kasasen wajen Faransa tace nan gaba kadan zata fara kwashe yan kasar ta daga jamhuriyar Nijar biyo bayan juyin mulki da sojoji sukayi a kasar.

Ofishin jakadancin Faransa a Yamai yace sakamakon rashin tsaro a kasar, hakan yasa ta shirya debe yan kasar ta daga Nijar din.

A makon da ya gabata ne sojoji suka yiwa shugaban kasar Bazoum juyin mulki.

Nijar ce kasa ta uku da aka yiwa juyin mulki a yankin Sahara,baya ga Burkina Faso da Mali a kasa da shekaru uku.

Lamarin ya sa kasashen ke kin jinin Faransa,tare da kulla alakar kut-da kut da kasar Rasha.

Comments (0)
Add Comment