Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sahalewa kudirin samar da cibiyoyin binciken magunguna, da bada horo a kwalejojin karatun likita 6 dake shiyyoyin kasarnan.
Bugu da kari Shugaba Buhari, ya amince da karin kudin hukumar na shekarar 2020 zuwa naira biliyan 7 da miliyan 5, sabanin naira biliyan 3 da yake a baya.
Babban sakataren hukumar TETfund, Farfesa Sulaiman Bogoro, shine ya bayyana hakan, yayin taron kwamatin amintattu na shekarar 2020 da aka gudanar a Abuja.
- Matsalar wuta na ƙara ƙamari a jihohin Kano da makwabta
- Hatsarin mota ya yi sanadiyar mutuwar aƙalla mutum 5 a Jihar Gombe
- An ƙaddamar da shirin rigakafin cutar Polio a yankin tafkin Chadi
- Nan da wata 6 yankin Arewacin Najeriya zai fitar da matsayarsa kan zaben 2027 – Hakeem Baba Ahmad
- An soki yadda aka kafa Kwamatin Kidaya a Najeriya
Yace amincewa batun ya baiwa hukumar TETFund damar gina dakunan gwaje gwajen cutuka masu yaduwa biyu a kowacce shiyyar kasarnan, abinda zai sanya hukumar ta zama gagara misali, wajen samar da cibiyoyin gwajin cutar corona a Nigeria.
Farfesa Bogoro ya kuma ce kwamatin amintattun hukumar, ya amince da zuba naira miliyan 200, domin daukar nauyin wasu jami’o’i dama hukumar NAFDAC wajen gudanar da bincike kan cutar corona.