A wani labarin kuma, Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya tana tantance kamfanonin cikin gida 19 domin samar da maganin gargajiyan da zai magance cutar corona.
Kamfanonin sun yi ikirari daban-daban, wadanda suka hada da samar da maganin cutar corona kai tsaye zuwa samar da maganin da zai warkar da alamun cutar.
Kamfanonin sun gana da shugabannin ma’aikatar tare da sashen kula da magungunan gargajiya.
- Akalla mutane 28 ne suka rasa rayukansu sanadiyyar hare-haren ‘yan bindiga a jihar Zamfara
- ‘Yan Kasuwa na nuna damuwar su kan faduwar farashin kayan Abinci
- Gwamnatin Jigawa ta bukaci jama’a da su kai rahoto kan duk dillalin da ke kokarin bata shirin Noma
- Hukumar JAMB ta cire wasu cibiyoyi guda 5 daga jerin wuraren gudanar da jarabawar UTME ta 2025
- Hukumar EFCC na neman jami’an CBEX ruwa a-jallo
Sai dai, an bukaci kamfanonin da su gabatar da samfurin magungunansu zuwa ga hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC, daga cikinsu za a zabi kamfanoni 3 wadanda za a tallafawa da kudade.
Karamin ministan lafiya, Sanata Adeleke Mamora, shine ya tabbatar da hakan yayin zantawa da manema labarai.