Gwamnatin jihar Niger ta bayar da sanarwar cewa Almajirai 64 da akayiwa gwaji ya nuna suna dauke da cutar COVID-19 a jihar, sun samu lafiya za’a kuma maida su zuwa ga iyayan su.
Kwamishinan lafiya da ayyukan asibitoci na jihar Dr Muhammad Makusidi shine ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyi daga wajan yan Jaridu a Minna.
Ya bayyana cewa wadanda ba yan asalin jihar bane an mayar da su zuwa jihohin su na asali.
- Majalisar Dokokin Legas ta sake zaɓen Obasa a matsayin kakakinta
- An yi garkuwa da wani ɗansanda a Abuja
- Gwamnatin Jihar Yobe ta bayar da tallafin karatu da ya kai Naira biliyan 2.22 ga dalibai 890
- Kungiyar NANS ta yi barazanar fara zanga-zanga a fadin Najeriya
- Kotun ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati tafiya kasashen waje don neman magani
Dr Muhammad ya kara da cewa kawo yanzu mutane 1,778 aka yiwa gwaji cikin su an samu mutane 166 da suka kamu da cutar.
Gwamnan jihar Abubakar Sani Bello a yayin ganawa da kwamitin karta kwana kan cutar COVID-19 a jihar bisa jagorancin Ibrahim Matane, ya umarci dalibai da ma’aikata su cigaba da kasancewa a gida biyo bayan cigaba da rufe makarantu da ofisoshi, sakamakon karuwar bullar cutar a jihar.